Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-06-19 10:36:23    
Kafofin yada labarai na Masar sun mai da muhimmanci sosai a kan ziyarar firaministan kasar Sin a kasar

cri
Daga ran 17 zuwa 18 ga wata, firaministan kasar Sin Wen Jiabao ya kai ziyarar aiki a kasar Masar. A lokacin ziyarar, kafofin yada labarai na Masar sun nuna kulawa sosai a kan ziyarar Mr.Wen, kuma sun ba da rahotanni da yawa dangane da ziyarar.

Jaridar Al-Gomhouria ta Masar ta ba da rahoto a ran 18 ga wata cewa, a lokacin ziyarar Wen, bangarorin biyu na Masar da Sin sun rattaba hannu a kan yarjejeniyoyin hadin gwiwa da takardar fahimtar juna da dama, kuma sun bude cikakken hadin gwiwa a tsakaninsu a fannin tattalin arziki da ciniki.

Bayan haka kuma, jaridar al-aharm ta kasar ta ba da sharhin da ke da lakabin 'makomar huldar abokantaka da ke tsakanin Masar da Sin', inda ta jaddada cewa, ziyarar Mr.Wen a Masar tana da muhimmanci sosai wajen inganta huldar da ke tsakanin kasashen biyu.(Lubabatu Lei)