A ran 12 ga wata a birnin Tehran, babban birnin kasar Iran, kakakin gwamnatin kasar Iran Gholam Hossein Elham ya bayyana cewa, kasar Iran tana yin nazari sosai a kan sabon shirin da kasashe 6 suka gabatar domin warware matsalar nulikiya ta Iran, haka kuma kasar Iran za ta ba da amsa a lokaci kuma yadda ya kamata, amma ba za ta yi shawarwari da ko wane a kan ikon gyara kayayyakin nukiliya ba.
A ran 12 ga wata, babban wakilin kungiyar EU da ke kula da manufofin diplomasiyya da zaman lafiya Javier Solana ya bayyana a kasar Luxembourg cewa, yana fata kasar Iran za ta ba da amsa ga wannan sabo shiri a cikin wannan mako.(Danladi)
|