Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-06-09 11:04:24    
Masu sha'awar kwallon kafa na Kasar Sin suna mai da hankali kan wasan Gasar kwallon kafa ta duniya ta 2006 da za yi a kasar Jamus

cri

Wakilin Kamfanin dillancin labarum Xinhua na kasar Sin ya ruwaito mana labari cewa , a ran 9 ga watan nan , za a bude wasan Gasar kwallon kafa ta duniya ta 2006 a kasar Jamus . Ko da ya ke Kungiyar wasan kwallon kafa ta kasar Sin ba za ta shiga wannan wasa ba , amma Masu sha'awar kwallon kafa na Kasar Sin suna mai da hankali sosai kan wasan .

Agogon Kasar Sin da na lasar Jamus suna da bambancin awa 6 , amma galibin masu sha'awar kwallon kafa za su duba gasa ta hanyar talabijin kai-tsaye . A cikin kungiyoyin da suke goyon baya akwai kungiyar Brazzil da Italy da Spain da Argentina da sauransu .

Kwanan baya yayin da Firayin minista Wen Jiabao na kasar Sin ya gana da Madam Angela Merkel , takwararsa ta kasar Jamus , ya bayyana cewa , shi ma mai sha'awar kwallon kafa ne . (Ado)