Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-05-14 20:38:00    
Kasar Iran ba za ta amince da shawarar daina harkokin nukiliya ba, in ji shugaban Iran

cri
Ran 14 ga wata, a birnin Tehran, shugaban kasar Iran Mr. Mahmoud Ahmadinejad ya bayyana cewa, idan kasashen Turai sun tanadi bukatar kasar Iran da ta daina harkokin nukiliya cikin lumana a cikin shawararsu, to, kasar Iran ba za ta amince da irin wannan shawara ba.

An labarta cewa, kasashen Birtaniya da Faransa da Jamus suna tsara sabuwar shawara kan batun nukiliya na kasar Iran, inda suka bukaci kasar Iran da ta yi hadin gwiwa da kasashen duniya, ta kuma daina harkokin tace sinadarin uranium, in ba haka ba, mai yiwuwa ne za a haddasa takunkumi. An yi kiyasta cewa, jami'an ma'aikatan harkokin waje na wadannan kasashe 3 da Mr. Javier Solana, babban wakilin kawancen kasashen Turai mai kula da manufar harkokin waje da zaman lafiya za su yi tattaunawa kan wannan sabuwar shawara a ran 15 ga wata.(Tasallah)