A ran 9 ga wata, Mr. Wu Bangguo, shugaban zaunennen kwamitin majalisar dokokin kasar Sin ya bayyana a nan birnin Beijing cewa, a shekarar da muke ciki, zaunennen kwamitin majalisar zai ci gaba da sa ido kan muhimman batutuwa da maganganun da ke jawo hankulan jama'a sosai. A sa'i daya kuma, zai kara yin wannan aiki ne a fili.
A wannan rana da safe, a gun taron shekara-shekara na majalisar dokokin kasar Sin, an saurari rahoton da Wu Bangguo ya gabatar a madadin zaunennen kwamitin majalisar. Mr. Wu ya bayyana cewa, a cikin shekarar da muke ciki, zaunannen kwamitin zai yi bincike kan yadda ake bin dokoki game da fannonin aikin gona da ikon mallakar fasaha da yin tsimin yin amfani da makamashin halittu da kuma aikin yin amfani da kasafin kudi da harkokin tattalin arziki. (Sanusi Chen)
|