Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-03-05 17:22:31    
Kasar Sin za ta mayar da kauyuka muhimman wuraren da za a zuba jari don raya manyan ayyukan wurin

cri
Firaministan kasar Sin, Wen Jiabao, ya bayyana a yau ran 5 ga wata a nan birnin Beijing cewa, gwamnatin kasar Sin za ta mayar da kauyuka muhimman wuraren da za a zuba jari wajen raya manyan ayyuka.

Wen Jiabao ya yi wannan furuci ne a yayin da yake bayani a kan aikin gwamnati a gun taron shekara shekara na majalisar wakilan dukan jama'ar kasar Sin, wato hukumar koli ta kasar Sin, wanda aka bude a ran nan. Ya ce, za a karfafa muhimman ayyukan gona a kauyukan kasar Sin, musamman ma bunkasa kananan ayyukan tsaren ruwa, haka kuma za a kara raya tsarin yaki da ambaliyar ruwa da bala'in fari, a sa'i daya kuma, za a kara raya manyan ayyuka a kauyuka, ciki har da gina hanyoyi da samar da ruwan sha da fitar da gas daga shara da bunkasa giza-gizan lantarki da sadarwa, haka kuma za a kara raya muhallin zaman rayuwar dan Adam. Bayan haka kuwa, za a karfafa ayyukan ba da ilmi da kiwon lafiya da al'adu da dai sauran harkokin jama'a a kauyuka. Ban da kara zuba jari ga kauyuka da ayyukan noma, gwamnati za ta kuma sa kaimi ga duk al'umma da su zuba jari a wajen kauyuka da kuma ba da jagoranci a kan batun.(Lubabatu Lei)