Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-03-02 21:44:38    
An share fagen taron shekara-shekara na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin sosai

cri

Bisa labarin da wakilanmu suka aiko mana, an ce, ya zuwa yanzu, an riga an share fagen taron shekara-shekara na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa da za a fara yi tun daga gobe, wato ran 3 ga wata.

A ran 2 ga wata ne, Wu Jianmin, kakakin wannan taro ya shelanta wannan labari a nan birnin Beijing. Ya bayyana cewa, a gun taron, membobi fiye da dubu 2 na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa za su kara ba da ra'ayoyinsu kan muhimman batuttukan da ke shafar tsari na shekaru 5 masu zuwa domin bunkasa harkokin tattalin arziki da jin dadin rayuwar jama'a. Bugu da kari kuma, za su halarci taron shekara-shekara na majalisar dokokin jama'ar kasar Sin bisa matsayin 'yan kallo, inda za su saurari tare da tattauna rahoton aiki da firayin minista Wen Jiabao zai gabatar a madadin gwamnatin tsakiya.

Wannan taro da za a rufe shi a ran 13 ga wata za a shafe kwanaki 10 ana yinsa a nan birnin Beijin. (Sanusi Chen)