Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-10-23 10:41:39    
Kasashe 8 na yammacin Afirka za su fitar da katin visa na bai daya a fannin yawon shakatawa

cri

Kasashen kungiyar kawancen tattalin arziki da kudi na yammacin Afirka guda 8 za su fitar da katin visa na bai daya a fannin yawon shakatawa don sa kaimi ga bunkasuwar yawon shakatawa ta kasashen dake cikin kungiyar.

A gun bikin rufe taron yawon shakatawa na duniya a karo na biyu da aka yi a Bamako, babban birnin kasar a ran 22 ga wata, ministan kula da harkokin sana'o'in hannu da yawon shakatawa na kasar Mali N'diaye Bah ya bayyana cewa, kasashe 8 na kungiyar suna yunkurin bullo da katin visa na bai daya a fannin yawon shakatawa a cikin 'yan shekarun nan don ba da taimako ga mutanen kasashen kungiyar dake tafiye-tafiye a kasashen cikin 'yanci, da kuma sa kaimi ga bunkasuwar sana'ar yawon shakatawa.

An kafa kungiyar kawancen tattalin arziki da kudi ta yammacin Afika a shekarar 1994, wadda ta hada da kasashen Benin da Burkina Faso da Cote D'ivoire da Mali da Nijer da Senegal da Togo da kuma Guinea Bissau.(Zainab)