Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-09-28 11:00:26    
An kaddamar da taron 26 kan yawan mutane na duniya a kasar Morocco

cri

A ran 27 ga wata da dare, an kaddamar da taro kan yawan mutane na duniya a karo na 26 a birnin Marrakech dake kudancin kasar Morocco. Masana da kwararru kan ilmin yawan mutane da kidayar jama'a fiye da dubu 2 da suka fito daga kasashe da yankuna 114 sun halarci taron. Wannan ne karo na farko da aka gudanar da taron a wata kasa dake nahiyar Afirka.

A taron kwanaki 5, masu halartar taron za su tattauna cikin kungiya-kungiya kan batutuwa fiye da dari 2 a game da makomar jama'ar duniya, ciki har da dangantaka tsakanin batun yawan mutane da sauye-sauyen yanayi, da tsakanin kaurar mutane a duniya da rikicin tattalin arziki, da kuma tsakanin yawan mutanen da aka Haifa da tsarin jin dadi na zamantakewar al'umma. An yi tattaunawa da nune-nune kan batutuwan da dama game da yawan mutane a wurin taron.(Zainab)