Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-11-11 12:59:11    
kasahen duniya sun nuna yabo ga shirin sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki da kasar Sin ta tsara yana da muhimmiyar na'ana

cri

Bayan gwamnatin kasar Sin ta fitar da matakai guda 10 a ran 9 ga wata don ci gaba da kara biyan bukatun cikin gida da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki lami lafiya, wasu shugabannin kasashen waje da kafofin watsa labaru sun mai da hankulansu a kan wadannan matakai kuma sun nuna yabo bi da bi.

A ran 10 ga wata, firayin ministan kasar Australia Mr.Kevin Rudd ya nuna cewa, matakai guda 10 masu sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki suna da muhimmiyar ma'ana, sun bayyana gwamnatin kasar Sin ta mai da hankalinta a kan bunkasuwarta a cikin gida. Kuma a ganninsa, wandannan matakai kyakyawan albishir ne ga tattalin arziki na kasar Australia da sauran yankuna na duniya.

Daily Telegraph ta kasar Birtaniya ta bayar da labarin cewa, a gannin masanan ilmin fannin tattalin arziki, wandannan matakai za su sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki na kasar Sin da ya karu da kashi biyu bisa dari a shekarar mai zuwa. Bankin Morgan Stanley na kasar Amurka ya bayyana cewa, wadannan matakai sun shaida cewa, gwamnatin kasar Sin tana son kara imani na kamfanonin masu zaman kansa ta hanyar yin alkawarin tabbatar da bunkasuwar tattalin arziki cikin sauri.(Abubakar)