2020-09-11 10:51:48 cri |
Ministan ayyukan jin kai da daidaita bala'u na kasar Lawan Magagi, ya bayyana cewa, gwamnati tana daukar matakan da suka dace, don sake tsugunar da wadanda bala'in ya shafa. A don haka tana bukaci bangarorin daban-daban na al'umma dake kasar, da su taimaka.
Galibi dai, lokacin damina a kasar ta Nijar, yana farawa ne, daga watan Yuli zuwa Satumban kowa ce shekara. A shekarar 2012 ma, kasar ta yi fama da matsalar ambaliyar ruwa, da ba a taba ganin irinta ba cikin shekaru 80, inda har mutane 88 suka sheka barzahu, baya ga masifu sama da dubu 500.(Ibrahim)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China