2020-08-05 10:43:47 cri |
Dr. Horton ya ce matakan kin jinin Sin na kara kazanta, inda a yanzu suke haifar da yanayi maras kyau, lamarin da ke haifar da nuna wariyar launin fata, da kin jinin wasu al'ummu, matakin da ke barazana ga zaman lafiya da tsaro a matakin kasa da kasa.
Jaridar Birtaniya ta "The Guardian" ta rawaito kalaman na Dr. Horton, yana mai cewa a wannan muhimmin lokaci, ya fi dacewa a maida hankali wajen aiki tukuru maimakon raunana kokari, a kuma kyautata cudanyar dukkanin sassa a fannin yaki da wannan annoba, da fadada fahimtar juna tsakanin al'ummu.
Daga nan sai ya bayyana Sin mai jama'ar da ta kai biliyan 1.4 a matsayin kasa da ita ma ke fuskantar kalubalen tattalin arziki, wanda ke addabar dukkanin duniya. A don haka bazuwar cutar COVID-19 a cewar Dr. Horton, ta haifar da bukatar hadin kan dukkanin al'ummun duniya, maimakon saka kafar wando daya tsakanin gwamnatoci. (Saminu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China