2020-08-03 14:20:33 cri |
Hukumar wadda ta yi gargadi game da farin, ta jaddada cikin rahotonta na baya-bayan nan cewa, ana gudanar da aikin sa ido a kasashe yadda ya kamata, sannan an shirya matakan dakile farin saboda samun gargadin wuri da aka samu da kuma matakan tunkararsu da FAO din ta tsara.
Sanarwar da hukumar ta fitar, ta ce an fuskanci barazanar da ba a taba gani ba kan wadatar abinci da rayuwar jama'a a gabashin Afrika, kuma ana yin dukkan mai yuwuwa wajen kare aukuwar makamanciyar matsalar a yankin Sahel, wanda a yanzu haka ke fuskantar matsaloli da dama. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China