2020-06-19 19:47:45 cri |
Alkaluman kididdiga sun nuna cewa, daga shekara ta 1990 zuwa karshen shekara ta 2016, an samu barkewar al'amuran ta'addanci fiye da sau dubu 1 a jihar Xinjiang, abun da ya haddasa mummunar hasarar rayuka da dukiyoyi. Amma duk da haka, akwai wasu 'yan siyasa gami da kafafen yada labaran kasar Amurka, wadanda suka jirkita gaskiya da boye ainihin abubuwan da suka faru, abun da ya sa kasa da kasa ba su san gaskiyar abubuwan dake faruwa ba. Abun takaici shi ne, wadannan 'yan siyasar ba su koyi darasi daga hare-haren ta'addanci na ranar 11 ga watan Satumba ba, har ma suke goyon-baya da tallafawa 'yan ta'addan da suka sha aikata kisan kiyashi a jihar. Zartas da shirin doka da ya jibanci Xinjiang, da bata sunan kasar Sin, da kuma kalubalantar manufofin gwamnatin kasar kan Xinjiang da Amurka ta yi, ya shaida cewa, Amurka tana marawa 'yan ta'addan baya, wannan ya nuna cewa, jirgi daya ne ya kwaso su!
Kafar talabijin ta CGTN ta taba bullo da wasu shirye-shirye biyu a karshen bara, wadanda suka shafi yadda ake dakile ayyukan ta'addanci a jihar Xinjiang, inda masu amfani da yanar gizo ta intanet suka maida martani cewa, shin irin wadannan munanan ayyukan ta'addanci su ma hakkokin dan Adam ne da Amurka take karewa? Gaskiyar abun da ya wakana a Xinjiang ita ce, 'yan ta'adda sun kashe fararen hula da dama! Amma wasu kafafen yada labaran kasashen yamma sun yi shiru, har ma akwai wasu shafukan sada zumunta wadanda suka cire wadannan shirye-shiryen biyu bisa hujjoji daban-daban. Yanzu CGTN ya bullo da sabon shiri, ko me za su yi a wannan karon? Ko za su ci gaba da yin shiru ne? Duniya ta zura musu ido!(Murtala Zhang)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China