2020-06-22 09:01:57 cri |
A ran 9 ga watan Yunin da muke ciki, sojojin kasar Sin wadanda suke tabbatar da zaman lafiya a kasar Lebanon, sun yi aikin jin kai na kawar da nakiyoyin kasa a yankin dake kan iyakar kasashen Lebanon da Isra'ila. Wannan ya alamta cewa, an farfado da aikin jin kai na kawar da nakiyoyin kasa, a yankin da rundunar wucin gadi ta MDD dake Lebanon ta dakatar da aikin har na tsawon shekaru 10 da suka gabata. (Sanusi Chen)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China