2020-06-01 14:12:34 cri |
Shugaban wanda ya bayyana haka, yayin da yake jawabi ta kafar rediyon kasar, yayin da ya ziyarci lardin a karshen mako, Ya ce, matakan da sojojin suke dauka suna haifar da kyakkyawan sakamako.
Ya ce, sun samu bayanan dake cewa, an kashe manyan dakarun dake adawa da gwamnati. Haka kuma fafatawar karshe da dakarun tsaron kasar suka yi tana da girma, sun kuma samu nasara. Shugaban ya ce, hukumomi na samun nasara a gundumomin Mocimboa da Quissanga da Muidumbe da kuma Macomia dake lardin Cabo Delgado, wuraren da 'yan ta'addan suke kai hare-haren
Shugaban wanda ministocin tsaro da na cikin gida suka rufa masa baya yayin ziyarar, ya kuma gana da manyan jami'an tsaron kasar dake lardin na Cabo Delgado. (Ibrahim)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China