2020-05-01 20:39:58 cri |
Masana sun bayyana cewa, manufofin kasar Sin na kawar da talauci da kokarin da take na inganta rayuwar mazauna yankunan karkaka, abu ne da ya dace kasar Namibia da ma nahiyar Afirka baki daya su yi koyi da su wajen magance matsalar rashin daidaito a cikin al'umma.
Mai sharhi kan harkokin jin dadin jama'a da siyasa a jami'ar Namibia Ndumbah Kwamwayah, ya bayyana cewa, "Ya dace mu yi koyi daga kasashe kamar kasar Sin, wadda ta inganta rayuwar al'umma ta hanyar raya da ma zamanintar da aikin gona wajen zuba jari mai yawan gaske a bangaren mazauna karkara. (Ibrahim Yaya)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China