Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Adadin wadanda suka kamu da cutar COVID-19 a Lagos ta Nijeriya ya tashi zuwa 100
2020-04-04 20:20:21        cri
Lagos, cibiyar hada-hadar kasuwanci ta Nijeriya, ita ce jihar da cutar numfashi ta COVID-19 ta fi shafa a kasar, inda aka samu rahoton mutane sama da 100 da suka kamu da cutar, tun bayan bullarta a kasar a ranar 27 ga watan Fabreru.

Rahoto na baya-bayan nan da cibiyar dakile yaduwar cututtuka ta kasar NCDC ta fitar jiya da daddare, ya nuna cewa, Lagos inda aka fara samun bullar cutar, na da jimilar mutane 109 da suka harbu.

Kawo yanzu, akwai mutane 210 da suka kamu da cutar COVID-19 daga jihohin kasar 14, ciki har da birnin tarayyar Abuja.

Kwamishinan lafiya na jihar Lagos, Akin Abayomi, ya bayyana yayin wani taron manema labarai jiya da dare cewa, hukumomi na bibiyar akalla mutane 2,450 da suka yi hulda da wadanda suka kamu da cutar.

Shugaban kasar Muhammadu Buhari ya ba da umarnin takaita zirga-zirga a jihar na tsawon makonni 2, matakin da ya ce an dauka ne bisa shawarar cibiyar NCDC da ma'aikatar lafiya ta kasar. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China