Harkoki a kasar Sin sun fara daidaita sannu a hankali, inda ake ci gaba da samun nasara a kokarin shawo kan cutar COVID-19 da kuma dakile ci gaba da yaduwarta. Kan haka ne wakiliyarmu Fa'iza Muhammad Mustapha, ta tattauna da Bello Jakada, wani dalibi dan Nijeriya dake karatu a birnin Fuzhou na kasar Sin, don jin halin da suke ciki yanzu. Ga yadda tattaunawar ta su ta kasance.