A daidai wannan lokaci da kasar Sin ke ci gaba da samun nasara a kokarin shawo kan cutar COVID-19 da kuma dakile ci gaba da yaduwarta, harkoki sun fara daidaita a hankali. Kan haka ne wakiliyarmu Fa'iza Muhammad Mustapha, ta tuntubi Ahmad Bala Alhassan, wani dalibi dan Nijeriya dake karatun digiri na 3 a jami'ar Jiaotong dake birnin Xi'an na kasar Sin, don jin halin da suke ciki yanzu. Ga kuma yadda tattaunawar ta su ta kasance.