2020-03-07 17:03:22 cri |
An kai wani harin kunar-bakin-wake kusa da ofishin jakadancin Amurka dake kasar Tunisiya a birnin Tunis, a jiya Jumma'a, lamarin da ya raunata mutane da dama.
Gidan talabijin na kasar Tunisiya ya ruwaito wata majiya daga bangaren tsaron kasar na cewa, da safiyar jiya Jumma'a, wasu 'yan kunar-bakin-wake biyu a kan babur, sun je wani shingen bincike dake kusa da ofishin jakadancin Amurka don kaddamar da harin, lamarin da ya yi ajalinsu nan take.(Murtala Zhang)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China