2020-02-26 20:57:24 cri |
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen Sin Zhao Lijian, ya ce Sin a shirye take ta yi hadin gwiwa da kasashen Japan da Koriya ta kudu, a yakin da ake faman yi da cutar numfashi ta COVID-19, tana da kuma aniyar samar da tallafi ga kasashen 2 gwargwadon karfinta a wannan fanni.
Zhao Lijian ya yi wannan tsokaci ne a yayin taron menema labarai da ya gudana a yau Laraba, lokacin da aka yi masa tambaya game da yanayin da ake ciki, game da yaduwar cutar a kasashen 2. Ya ce Sin na yin duba na tsanaki game da yaduwar cutar a kasashen 2. (Saminu Hassan)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China