Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kada a bata kokarin da ake yi na shawo kan cutar coronavirus ta hanyar jita-jita
2020-02-09 20:32:06        cri

Babban darektan hukumar kiwon lafiya ta duniya(WHO) Mr.Tedros Adhanom Ghebreyesus a jiya 8 ga wata ya bayyana cewa, hukumar WHO tana kokarin fafatawa da masu mayar da hannun agogo baya wadanda ke ta yada jita-jita, baya ga kokarinta na dakile yaduwar cutar numfashi da kwayar cutar coronavirus ke haddasawa. Ya jaddada cewa, rashin gaskiyar bayanan da ake yadawa zai kara wahalar aikin ma'aikatan lafiya, tare da haifar da rudani da kuma tsoro ga al'umma. A saboda haka, hukumar WHO na kafa wata tawagar samar da bayanan gaskiya, don karyata jita-jitar. Hakika, furuci da matakan da hukumar ta dauka suna da muhimmiyar ma'ana ta fannin hana yaduwar jita-jita da kuma wadanda ke yunkurin lalata kokarin da ake yi na dakile cutar.

Tun bayan barkewar cutar, gwamnatin Sin ba ta bata lokaci ba, inda nan take ta gudanar da bincike, da gano ainihin nau'in kwayar cutar, gami da bayyanawa WHO, da sauran kasashe yadda wannan kwayar cutar take. Baya ga haka, ta dauki kwararan matakai na dakile yaduwar cutar, matakan da suka samu amincewa da goyon baya daga kasa da kasa. Duk da haka, wasu 'yan siyasa da kafofin yada labarai na kasashen yammaci suka yi ta samar da labaran da ba na gaskiya ba, don shafawa kasar Sin bakin fenti, matakan da suka keta hakkin Sinawa mazauna ketare, wadanda kuma suka kawo cikas ga hadin gwiwar kasa da kasa ta fannin shawo kan cutar.

Kwayoyin cuta abokan gaba ne ga 'yan Adam baki daya. Yadda kasar Sin ke daukar kwararan matakai na dakile yaduwar cutar, ba ma kawai don kare al'ummarta ba ne, har ma don kare al'ummar duniya baki daya.(Lubabatu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China