Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sin na sanya ido sosai bayan karuwar masu kamuwa da wata cutar numfashi
2020-01-20 16:03:21        cri
Yanzu haka karin biranen kasar Sin na daukar matakan sanya ido, da na kandagarki, bayan bullar wata cutar numfashi da a yanzu haka, hukumomi ke cewa yawan masu fama da ita suna karuwa.

A birnin Wuhan inda cutar ta fara bulla, ya zuwa ranar Asabar din karshen makon jiya, mutane 3 sun rasu sakamakon kamuwa da cutar. Kaza lika yawan sabbin wadanda suka kamu da ita ya kai mutum 136, tsakanin ranekun Asabar da Lahadin karshen mako, kamar dai yadda hukumar lafiya ta yankin ta sanar. Hukumar ta ce kafin ranar Asabar din, masu dauke da cutar na fama da zazzabi, da tari, da shakewar kirgi.

An dai samu mutane 2 dake dauke da wannan cuta mai nasaba da sanyin hakarkari ko "pneumonia" a birnin Beijing, da kuma mutum guda a birnin Shenzhen, a karon farko tun bayan da cutar ta bayyana a Wuhan. An kuma ce a baya bayan nan, dukkanin mutanen 3 sun yi balaguro zuwa birnin na Wuhan. (Saminu Hassan)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China