2020-01-02 07:29:55 cri |
Makiyayan wasu sassan birnin Naqu na jihar Xizang ne suke yin kaura zuwa sabbin gidajensu. A kwanakin baya, gaba dayan makiyayan 2900 da suka fito daga birnin sun yi ban kwana da gidajensu dake da tsayin mita 5000 daga leburin teku, kuma sun yi tafiyar kusan kilomita dubu zuwa sabbin gidajen da aka samar musu a gundumar Gongga dake kudancin gabar kogin Yarlung Zangbo, inda ake samun sassaucin tsayin leburin teku. Kaurar na daga cikin ayyukan da aka gudanar a jihar cikin shekarun baya na kaurar da mazauna wasu sassan dake da tsananin tsayi daga leburin teku, don sassauta wahalar rayuwarsu.(Lubabatu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China