Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasashen duniya na kara cin moriya daga manufar kasar Sin ta kara bude kofa ga kasashen waje
2019-12-26 20:35:56        cri

Babban gidan rediyo da talabijin na kasar Sin ko kuma CMG a takaice ya bada wani sharhin yau Alhamis, mai taken "kara bude kofa ga kasashen waje da kasar Sin take yi na kara samarwa duniya alheri".

Sharhin ya ce, a shekarar dake dab da karewa wato 2019, bude kofa ga kasashen waje wani muhimmin fanni ne na ci gaban kasar Sin, wanda kuma dalili ne da ya sa kasar Sin take iya kara samarwa duniya alheri.

A cewar sharhin, a bana, yayin da ra'ayin bada kariya ga harkokin kasuwanci da ra'ayin nuna bangaranci ke ci gaba da yaduwa a duk fadin duniya, kasar Sin na ci gaba da zurfafa bude kofarta ga kasashen waje a fannonin musayar kayayyaki da inganta ka'idoji, da kara samun kwarewa domin tinkarar hadari da kalubale. Kasar Sin dake fadada bude kofarta ga kasashen ketare na kara samar da alheri da moriya ga duk fadin duniya.

Har wa yau, sharhin ya ce, a sabon zamanin da muke ciki, ya kamata Sin ta fadada bude kofar kasuwanninta, da kyautata yanayin kasuwanci, da zurfafa hadin-gwiwar bangarori daban-daban, da ci gaba da inganta ayyukan shawarar "ziri daya da hanya daya", a wani mataki na sanya sabon kuzari ga ci gaban tattalin arzikin duniya.(Murtala Zhang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China