Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Yan fashin teku sun yi garkuwa da mutane 4 a Gabon
2019-12-23 13:48:54        cri
A daren jiya Lahadi, gwamnatin kasar Gabon ta sanar da cewa, 'yan fashin tekun sun kai hare-hare ga jiragen ruwa na Libreville, babban birnin kasar guda hudu, lamarin da ya haddasa rasuwar mutane guda 1, tare da yin garkuwa da ma'aikatan jiragen ruwa guda hudu.

Jami'in mai kula da harkokin cikin gidan kasar, ministan harkokin labarai, kana kakakin gwamnatin kasar Gabon Edgard Anicet Mboumbou Miyakou, ya bayyana bayan taron gaggawa da aka yi cewa, sojojin kasar sun isa wurin nan take, a lokacin da suka samu labarin aukuwar lamarin, kuma bisa taimakon da 'yan sandan kasa da kasa suka samar musu, a halin yanzu, an kawar da kalubale a wannan yankin teku, kuma suna ci gaba da neman wadanda aka yi garkuwa da su. An kuma bayyana cewa, gwamnatin kasar za ta fara bincike kan wannan harka.

A halin yanzu kuma, 'yan jaridar kamfanin dillancin labarai na Xinhua, suna dukufa wajen tabbatar da asalin mutane 4 da aka yi garkuwa da su. (Maryam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China