2019-12-12 14:00:03 cri |
Haka kuma, ya ce, babban ci gaba da kasar Sin ta samu cikin shekaru da dama da suka gabata abun burgewa ne kwarai da gaske. Ya ce kasar Sin tana mai da hankali kan aikin kawar da talauci, wanda ya dace da burin MDD cikin jadawalin neman dauwamammen ci gaba ya zuwa shekarar 2030. Ban da haka kuma, kasar Sin tana taimaka wa kasashe masu tasowa wajen gina asibitoci, da inganta fasahohin ayyukan gona, da kuma taimaka musu wajen kyautata yanayin hakkin dan Adam, ciki har da wasu kasashen Afirka. Bugu da kari, kasar Sin ta ci gaba da karfafa mu'amalar dake tsakaninta da kasashe masu tasowa, lamarin da zai ba da taimako ga sauran kasashe masu tasowa, wajen samun ci gaba kamar yadda kasar Sin ta samu. (Maryam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China