Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kafafen yada labarai sun ce: Maharin da ya dabawa wasu mutane wuka a birnin London na da alaka da kungiyoyin 'yan ta'adda
2019-11-30 16:10:21        cri
Rahotanni daga kafafen yada labarai sun ruwaito a jiya cewa, maharin da ya kai harin wuka a gadar birnin London, dan ta'adda ne da ake saki a baya-bayan nan, kuma yana da alaka da kungiyoyin 'yan ta'adda.

Rahotannin sun ce 'yan sandan Birtaniya sun san mutumin da ake zargi kuma an yi ammana yana sanye da alamar gidan yari.

Bayan aukuwar harin, 'yan sandan birnin London sun ayyana shi a matsayin harin ta'addanci.

'Yan sandan sun kuma harbe mutumin da ake zargi da dabawa mutane wuka a kan gadar birnin London dake cibiyar birnin a jiya Juma'a.

'Yan sandan sun yi ammana cewa mutumin da ake zargin na dauke da ababen fashewa a jikinsa.

Maharin ya kashe fararen hula 2 yayin da wasu 3 ke asibiti, sanadiyyar daba musu wuka da ya yi.

Biyo bayan harin, Firaministan Birtaniya Boris Johnson, ya ce za a kara girke 'yan sanda a tituna. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China