2019-10-29 10:54:40 cri |
Majalisar wakilai ta kasar Burtaniya ta zartas da wani daftari a ranar 19 ga wata, inda ta tsawaita lokacin kada kuri'u kan sabuwar yarjejeniyar ficewar kasar Burtaniya daga kungiyar EU, wadda firaministan kasar Boris Johnson ya kulla da kungiyar EU, kuma ta bukaci Boris Johnson da ya mika sakon ga kungiyar EU domin sake tsawaita aikin ficewar kasa daga kungiyar EU.
A wannan rana kuma, firaminista Johnson ya gabatar da sakon ga Donald Tusk, domin neman iznin tsawaita ranar ficewar kasar Burtaniya daga kungiyar EU daga ranar 31 ga watan Oktoban bana, zuwa ranar 31 ga watan Janairun shekarar 2020. (Maryam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China