Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Mahukuntan Afirka na kokarin rage kudaden harajin dake sulalewa
2019-10-25 20:38:14        cri
Hukumar kula da harkokin kudaden haraji ta Afirka (ATAF) ta bayyana cewa, ta samar da hidimomi na shawarwari da ma horo ga mambobinta, a kokarin ganin an rage kudaden harajin dake sulalewa ta hanyoyin da ba su kamata ba, a daidai lokacin da hukumomin tattara kudaden harajin Afirka ke shirin bikin cika shekaru 10 da kafa babbar hukumar ta ATAF

Wakiliyar kasar Uganda a hukumar ta ATAF Stella Nyapendi ce ta bayyana hakan, yayin zantawa da manema labarai a jiya Alhamis. Tana mai cewa, an kafa hukumar ATAF mai mabobin kasashe 38 ne, yayin da ake fargabar rikicin kudade na duniya na shekarar 2008, ka iya shafar tallafin kudaden da kasashen da suka ci gaba ke baiwa kasashen nahiyar.

Ana ganin hukumar a matsayin kungiya mafi girma a nahiyar, dake kula da batutuwan kudade haraji a duniya dake shafar nahiyar.(Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China