2019-10-24 09:59:04 cri |
Yayin da yake hira da wakilin kamfanin dillancin labarai na Xinhua na kasar Sin, kakakin kwamitin zabe mai zaman kansa na kasar Botswana, Osupile Maroba, ya ce an gudanar da zaben a wurare daban daban na kasar lami lafiya, karkashin sa idon da tawagogin kungiyar tarayyar Afirka AU da kungiyar raya kudancin Afirka SADC suka yi.
Zaben na wannan karo shi ne irinsa na 12 da ya gudana tun bayan da Botswana ta samu 'yancin kai a shekarar 1966. (Bello Wang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China