2019-10-20 16:43:34 cri |
Godwin Emefiele, gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), ya bayyana hakan ne a lokacin gabatar da rahoton babban bankin game da daidaita harkokin kudaden kasar na shekarar 2018, wanda aka baiwa kwafin sanarwa ga kamfanin dillancin labarai na Xinhua a Legas a jiya Asabar.
A cewar rahoton baya bayan nan na hukumar kididdiga ta kasar wato NBS, farashin kayayyaki a kasar ta yammacin Afrika ya karu da kashi 11.24 a watan Satumbar 2019, inda ya karu da 0.22 idan an kwatanta da watan Augasta.
Game da matakin karfin tattalin arzikin GDP kuwa, Emefiele yace, matsayin GDPn ya karu, hakan kuwa ya biyo bayan nasarorin da aka samu ne wajen fadada hanyoyin kudaden shiga wadanda basu shafi albarkatun man fetur ba, a yunkurin da gwamnatin Najeriyar ke yi na fadada tattalin arzikin kasar da kuma bunkasa hanyoyin samun kudaden shigar kasar.
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China