2019-09-18 14:04:31 cri |
Jami'in na kasar Sin ya bayyana hakan ne, lokacin da ya ziyarci gwamnan jihar Lagos, Mr Babajide Sanwo-Olu jiya Talata.
A nasa bangare, Gwamna Sanwo-Olu ya ce, manufar shirin raya kasa na gwamnatinsa, ita ce, samarwa al'ummomin jihar ingancin rayuwa da ci gaban tattalin arziki. A cewarsa, koda yake jihar tana fama da kalubale na karuwar yawan jama'a, duk ha haka, gwamnatinsa ta shirya horas da jama'a da samar musu sana'o'i na dogaro da kai.
Gwamna Sanwo-Olu ya kara da cewa, gwamnatinsa, za ta fadada alakarta da gwamnatin kasar Sin wajen gina al'umma ta hanyar samarwa matasan jihar damammaki na samun horo a fannoni daban-daban, ciki har da fasahar keke-kere, da aikin gona, da samar da kayayyaki da gine-gine da musayar al'adu.(Ibrahim)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China