2019-09-18 09:23:12 cri |
Cikin wata sanarwa da majalisar kungiyar ta fitar jiya Talata a birnin Monrovia na kasar Liberiya, kungiyar ta bayyana cewa, shawarar gwamnatin Najeriya ta rufe kan iyakokin nata, zai ci gaba da haifar da barazana wajen aiwatar da yarjejeniya game da zirga-zirgar jama'a cikin 'yanci a shiyyar.
A watan da ya gabata ne, hukumomin Najeriya suka sanar da rufe kan iyakokinsu da Benin da kuma Nijar a baya-bayan nan, a wani mataki na magance matsalar sumoga.
Majalisar ECOWAS dai ta ce, matakin na iya kawo cikas, wajen cimma babbar manufar kungiyar, da suka hada da samar da kyakkyawar makoma, budewa kasashen yankin yammacin Afirka iyakokin juna, mai cike da zaman lafiya da kwanciyar hankali.(Ibrahim)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China