2019-09-13 16:25:34 cri |
Yayin taron kungiyar na 16 da ya gudana a birnin Abu Dhabi fadar mulkin hadaddiyar daular larabawa, kwamitin ministoci mai aikin sanya ido na kungiyar ko JMMC a takaice, ya amince da daukar wannan mataki.
Yayin taron, kasar Saudiyya ta ce za ta daidaita yawan man da take fitarwa zuwa ganga miliyan 9.89 a ko wace rana, daga watan Oktoba mai zuwa, yayin da kasashen Iraqi da Najeriya suka amince da kara rage yawan man da suke fitarwa.
Cikin wata sanarwa da kwamitin na JMMC ya fitar, ya jaddada muhimmancin ci gaba da aiwatar da matakan hadin gwiwa, a fannin daidaita farashin danyen mai a kasuwannin duniya. (Saminu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China