2019-08-26 10:42:33 cri |
Sanarwar ta kara da cewa, aikin da tawagar tallafin kiwon lafiyar ta kasar Sin ta gudanar a kasar Eritrea ya kara bayyana kakkarfar dangantakar hadin gwiwa dake tsakanin kasashen biyu.
Tawagar kiwon lafiyar ta kasar Sin, ta kunshi likitoci, wadanda suka samar da aikin jiyya kyauta ga jama'ar kasar Eritrea a tsawon shekara guda, sun kammala aikinsu a ranar Asabar. Kwararrun likitocin Sinawa sun gudanar da ayyukan kiwon lafiya ne a asibitoci daban daban a kasar Eritrea.
A cewar ofishin jakadancin kasar Sin a Eritrea, sama da likitoci sinawa da sauran kwararrun jami'an kiwon 200 ne suka gudanar da aikin jiyya kyauta a kasar Eritrea tun daga shekarar 1997. (Ahmad Fagam)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China