2019-08-21 21:29:58 cri |
A hakika, wasu manyan jami'an gwamnatin Amurka da kuma hukumomin da suka hada da hukumar leken asiri ta kasar suna mara baya ga masu tsattsauran ra'ayi a Hong Kong, wadanda baya ga saduwa da 'yan aware na Hong Kong, suna kuma ba su kudade da ma shawara, har ma suka yi barazanar alakanta batun Hong Kong da batun takaddamar cinikiyya dake tsakanin Amurka da Sin.
Tun a watan Yunin wannan shekara, masu tsattsauran ra'ayi da nuna karfin tuwo sun kaiwa 'yan sanda hari, da kuma dukan 'yan jarida da masu yawon shakatawa, har ma sun wulakanta tutar kasar Sin da tambarin kasar da na yankin musamman na Hong Kong, sun kuma toshe hanyoyi da kawo tseko a filin jirgin saman yankin…
A game da wannan, tsohon babban editan jaridar Wirtschaftswoche ta kasar Jamus, Stefan Baron ya wallafa wani sharhi a jaridar Handelsblatt, inda ya ce, "Idan irin haka ya faru a kasar Amurka, da tuni an kawo karshen tarzomar."
Bai kamata wasu 'yan siyasa da masu kin jinin kasar Sin su rika raina aniyyar gwamnatin kasar Sin da ma al'ummarta na kiyaye 'yanci da tsaro da dinkuwar kasar ba. Duk wanda yake neman lalata ci gaba da kwanciyar hankali a Hong Kong a yunkurin dakile ci gaban kasar Sin, lalle hakarsa ba za ta cimma ruwa ba. Sai dai ma kaikayi ya koma kan mashekiya. (Lubabatu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China