Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kwararrun kasashen Larabawa sun ce manufar gwamnatin Amurka na kara buga haraji ta shaida ra'ayinta na bada kariya ga harkokin cinikayya
2019-05-26 17:13:00        cri
A kwanakin baya ne, kasar Amurka ta dauki matakin karawa Sin harajin kaso 25 daga kaso 10 bisa dari, kan kayayyakinta da darajarsu ta kai dala biliyan 200, da matsawa wasu kamfanonin kasar Sin lamba, da nuna fin karfinta a harkokin kasuwancin duniya. Game da haka, wasu kwararru da masana daga kasashen Larabawa sun bayyana ra'ayoyinsu cewa, irin matakin da gwamnatin Amurka ta dauka na kara buga haraji kan hajojin kasar Sin ya shaida ra'ayinta na bada kariya ga harkokin kasuwanci, mataki ne kuma da ba zai kawo moriya ga kowace kasa ba.

Wani kwararre dan kasar Lebanon kan batutuwan kasar Sin Mahmoud Raya, ya ce, yayin da take mu'amala da sauran kasashe, Amurka ta kan dauki matakan sanya takunkumin tattalin arziki da kara buga haraji kan hajojin sauran kasashe, da nufin kawo cikas ga cigaban sauran kasashe. Tankiyar cinikayyar kasashen Sin da Amurka ta riga ta yi babbar illa ga masana'antun kasashen biyu da na sauran kasashe masu ci gaban masana'antu, haka kuma akwai yiwuwar samun raguwar bukatun man fetur a duniya, abun da zai kara haifar da abubuwan rashin sanin tabbas ga tsarin tattalin arzikin kasashen Larabawa.

A nasa bangaren, kwararre kan batun kasar Sin na kasar Masar, Samy El Kamhawy na ganin cewa, matakan da gwamnatin Amurka ta dauka na bada kariya ga harkokin kasuwanci da kara buga haraji kan hajojin sauran kasashe zai iya lahanta tattalin arzikin duniya.(Murtala Zhang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China