Ba a gina gida da gundume daya
2021-05-07 19:48:30 CRI
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taba tsamo wani karin magana da ta shahara a kasashen Afirka, wato “Ba a gina gida da gundume daya.” Don bayyana wajibcin hadin gwiwa tsakanin kasashe daban daban dake duniyarmu.
Kana a jiya Alhamis, yayin da shugaban na kasar Sin yake tattaunawa da sakataren janar na MDD, Antonio Guterres, ya sake yin kira don a ingiza huldar kasashe daban-daban. A cewarsa, mawuyacin halin da duniyarmu ta tsunduma ciki a halin yanzu, ya sa ya zama wajibi a kara inganta tsarin huldar kasashe daban-daban. (Bello Wang)