Sin:Zaman da majalisar wakilan Amurka ta kira game da batun Xinjiang adawa ce da kasar Sin
2021-05-07 19:47:08 CRI
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya shaidawa taron manema labarai da aka saba shiryawa Jumma’ar nan cewa, kwamitin harkokin wajen majalisar wakilan Amurka, ya gudanar da wani zama game da batun wai “kisan kare dangi kan ‘yan kabilar Uygur da sauran kananan kabilu a Xinjiang” ba tare da gabatar da shaidu ba.
Wang Wenbin ya kuma bukaci bangaren Japan, da ya kula da matsalar zubar da ruwan dagwalon tashar nukiliyar Fukushima, ya kuma bari kasashen duniya su sanya ido.(Ibrahim)