Adadin al’ummun Afirka da aka tabbatar sun harbu da COVID-19 ya haura miliyan 4.29
2021-04-08 10:13:11 CRI
Cibiyar kandagarki da yaki da cututtuka ta Afirka ko Africa CDC, ta sanar da cewa, ya zuwa tsakar ranar jiya Laraba, adadin wadanda suka harbu da cutar numfashi ta COVID-19 a nahiyar ya kai mutane 4,291,017.
Africa CDC, kwararriyar hukumar lafiya ta kungiyar tarayyar Afirka AU, ta ce adadin mutanen da cutar ta hallaka a nahiyar ya kai 114,344, yayin da mutane 3,858,461 suka warke daga cutar a duk fadin nahiyar.
Kawo yanzu, Afirka ta kudu, da Morocco, da Tunisia, da Habasha da Masar ne ke kan gaba, wajen yawan mutane da suka harbu da wannan cuta a nahiyar, kamar dai yadda cibiyar ta Africa CDC ta tabbatar.
Bisa alkaluman cibiyar, adadin wadanda suka harbu da cutar a Afirka ta kudu ya kai mutane 1,552, 853, ita ce kuma kan gaba a nahiyar. Sai kuma kasar Morocco mai mutane 499,025, da Tunisia mai 263,043. (Saminu)