An samu sabbin wadanda suka harbu da COVID-19 117 a babban yankin Sin
2021-01-25 11:02:47 CRI
Rahotanni daga hukumar lafiya ta kasar Sin, na cewa a jiya Lahadi an samu sabbin wadanda suka harbu da cutar numfashi ta COVID-19 124 a babban yankin kasar, cikin su 117 sun harbu da cutar ne a cikin gida, kana mutane 7 sun shigo da ita ne daga ketare.
Game da wadanda cutar ta harba a cikin gida, hukumar ta ce akwai mutane 67 da aka samu a Jilin, da 35 a Heilongjiang, da 11 Hebei, da mutane 3 a birnin Beijing, kana da mutum 1 a Shanghai, wanda aka ce ya sauka a Shanghai din ne daga wajen kasar.
Sai dai kuma hukumar lafiyar ta ce ba a samu rasuwar ko da mutum guda, sakamakon harbuwa da cutar ba.
Ya zuwa jiya Lahadi, jimillar wadanda cutar ta COVID-19 ta harba a kasar Sin ya kai 89,115, ciki hadda mutum 1,850 da har yanzu ke samun kulawar jami’an lafiya, kana cikin adadin akwai 109 dake cikin matsanancin yanayi. (Saminu)
Labarai Masu Nasaba
- Yawan mutanen da aka tabbatar sun kamu da COVID-19 a nahiyar Afrika ya zarce miliyan 3.41
- Masar ta fara yi wa jami’an lafiya alluran rigakafin COVID-19 na kamfanin Sinopharm
- Morocco ta amince da amfani da rigakafin COVID-19 na Sinopharm a matakin gaggawa
- Africa CDC ta bukaci kasashen nahiyar su tsaurara matakai yayin da annobar COVID-19 ke kara yaduwa