logo

HAUSA

WHO:Sayen alluran rigakafin COVID-19 fiye da yadda ake bukata da manyan kasashe ke yi ka iya tauye kokarin Afrika na yakar cutar

2021-01-22 11:23:26 CRI

WHO:Sayen alluran rigakafin COVID-19 fiye da yadda ake bukata da manyan kasashe ke yi ka iya tauye kokarin Afrika na yakar cutar_fororder___172.100.100.3_temp_9500049_1_9500049_1_6012_22239470-92c0-40f0-a694-6b102035e818

Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta ce yakin da nahiyar Afrika ke yi da cutar COVID-19 ka iya fuskantar koma baya, saboda rashin samun isassun alluran riga kafi, sanadiyyar sayewa da manyan kasashe ke yi.

Daraktar hukumar a Afrika, Matshidiso Moeti, ta ce yadda manyan kasashe ke saye alluran riga kafin, ka iya rage damar samunta a nahiyar ta Afirka, sannan zai tauye kokarin da ake na dakile annobar.

Kididdigar hukumar, ta nuna cewa, kawo yanzu, an yi amfani da alluran miliyan 40 a kasashe 50 mafiya arziki, yayin da a nahiyar Afrika, mutane 25 kadai aka yi wa a kasar Guinea. (Fa’iza Mustapha)

Fa’iza Mustapha