logo

HAUSA

Tyson Fury Zai Ba Wa Anthony Joshua Mamaki

2021-01-15 16:26:26 CRI

Tyson Fury Zai Ba Wa Anthony Joshua Mamaki_fororder_u=4108451840,3790059220&fm=26&gp=0

Ban Yi Nadamar Kulla Yarjejeniya Da Arsenal Ba, Inji Ozil

Duk da tata-burza da take tsakanin Dan wasa Mesut Ozil da Mikel Arteta, sai gashi dan wasa Ozil ya fayyace cewa, baya nadamar kulla yarjejeniya da kungiyarsa, Arsenal da kawo yanzu ya shafe akala shekaru 7 tare da ita.

Ozil ya sauya sheka daga Real Madrid zuwa Arsenal A shekarar 2013 kan kudi fam miliyan 42 da rabi, inda kuma a tsawon lokacin da suke tare ya taimakawa kungiyar wajen lashe kofunan FA 3, da na Community Shield 1, haka zalika ya lashe kyautar dan wasa mafi kwazo a kakar wasa ta 2015/2016.

Sai dai daga bisani, tauraron Dan wasan tadaina haskawa, musamman lokacin da Sabon mai horaswa na kungiyar ya zo, Mikel Arteta.

Amma duk da wannan, Ozil yace bai taba yin nadamar kulla yarjejeniya da Arsenal ba.

Shekaru 10 Da Kafa Babban Tarihi A Barcelona

Ranar 10 ga watan Janairun shekara ta 2011, ‘yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Barcelona suka zama kan gaba a jerin wadanda zasu lashe kyautar gwarzon dan kwallon kafa na duniya wato Ballon d’Or.

Lionel Messi ne ya zama zakara a shekarar, ya yin da takwaransa Davi Hernandez dan kasar Sipaniya ya yi na biyu, sai daya dan uwan nasu, Andres Iniesta wanda shima dan Sipaniya ne ya yin na uku a shekarar.

A lokacin Barcelona tana kan ganiyarta ta lashe wasanni da kuma kofuna domin watanni shida tsakani ta lashe gasar cin kofin zakarun turai wato Champions League kuma na hudu a tarihin kungiyar.

A shekarar 2011, Messi da Davi da Iniesta ne suka mamaye kyautar Ballon d’Or ta gwarzon dan kwallon duniya kuma Messi ya fara lashe kyautar Ballon d’Or a shekarar 2009 da 2010 da 2011 da 2012 da kuma 2015.

Ranar Asabar Barcelona ta je ta casa Granada a wasan mako na 18 da ci 4-0 wasan da dan wasa Griezmann ya zura kwallaye biyu a raga sannan kaftin din kungiyar Messi shima ya zura kwallaye biyu a fafatawar.

Tyson Fury Zai Ba Wa Anthony Joshua Mamaki – Cewar Pulev

Dan wasan damben nan, Kubrat Pulev, ya bayyana cewa yana da tabbacin cewa dan wasa Tyson Fury zai doke Anthony Joshua a fafatawar da ‘yan birtaniyan biyu zasu yi nan gaba a cikin wannan shekarar.

A farkon watan Disambar daya gabata ne dai Anthony Joshua, ya doke Pulev a wani dambe da suka fafata a birnin Landan, wanda hakan yasa yanzu ake ganin mutum daya ne zai iya takawa Anthony Joshua birki, wato Tyson Fury.

Sai dai shima tuni Anthony Joshua, ya bayyana cewa shima ya gama shiryawa domin fafata wasa da Tyson Fury, dan burtaniya, a wasan da zakarun biyu zasu kece a sabuwar shekarar nan da muke ciki.

A ranar da Pulev yasha kashi a hannun Joshua, Tyson Fury ya bayyana cewa ya shirya tsaf domin fafata wasan Dambe da zakaran wannan lokacin Anthony Joshua a wasan da ake saran za’a fafata a birnin Landan din Ingila.

A tsakiyar wannan watan  ne dan damben Burtaniya Anthony Joshua ya doke Kubrat Pulev, dan asalin kasar Bulgeria wanda hakan ya kara fitowa da batun karawarsa da Tyson Fury fili kuma Joshua ya yi nasara ne a fafatawar da aka kai zagaye uku ana yi.

‘Yan kallo 1,000 ne dai aka bai wa damar shiga filin wasa na Wembley Arena, la’akari da daukar matakan bayar da tazara saboda annobar korona kuma jim kadan bayan nasarar da Anthony Joshua ya samu ne magoya bayansa suka rika fadar cewa ‘saura Fury’.

‘Yan kallo 1,000 ne aka baiwa damar shiga filin wasa na Wembley Arena, la’akari da daukar matakan bada tazara saboda annobar Korona sai dain idan ba’a manta ba kadan ya rage ganiyar Joshua ta ruguje a watan Disambar bara, a lokacin da ya dauki fansa kan Andy Ruiz Jr.

Kuma kisan da ya yi wa Kubrat Pulev a daren Asabar ya nuna cewa a yanzu Tyson Fury ne kawai ya rage su saka zare, don ya tabbatar wa duniya kololuwar inda kwarewarsa ta kai a duniyar dambe.

Anthony Joshua Murdadde ne na kin karawa, hannayensa cike suke da damatsa, sannan yana magana da murya mai sanyi, hade da murmushi a fuskarsa sannan a fagen dambe, yana da tarihin yiwa abokan karawarsa kwaf daya, yana da sunaye iri-iri na jarumta, abin da ke nufin cewa ga mutane da dama, Joshua ne gagarabadau cikin yan damben da suka fito daga Najeriya tun bayan gwarzon NBA Hakeem Olajuwon.

Tuni Joshua ya fara shafar rayuwar samari da yawa musamman a kudu maso yammacin Najeriya, kamar Legas babban birnin kasuwancin kasar domin da yawa daga cikinsu sun kalli yadda ya zama shahararre ya cika burinsa na rayuwa, kuma labarinsa kusan yazo dai-dai da nasu, na wanda ya sha wahalar rayuwa kafin daga bisani kofar arzikinsa ta bude ya sha kwana.

Labarinsa, wani abu ne da aka jima ana nuna irinsa a fina-finai irin na Nollywood, kamar dai ace na mutumin da burinsa na rayuwa ya cika bayan shan kwarba shekara da shekaru sannan Joshua ya zama wata sila ta samun karvuwar harkar dambe a Najeriya, domin a yanzu, har ta kai ga ana horar da mutane wasan a makarantu bayan tashi daga karatu, da kuma ranakun hutu da sauran wurare da dama.