in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Libiya ta yi na'am da kiran EU na dakatar da bude wuta
2019-05-16 10:15:47 cri
Gwamnatin kasar Libiya mai samun goyon bayan MDD, ta yi na'am da kiran kungiyar tarayyar Turai ta EU, game da bukatar dakatar da bude wuta a birnin Tirabulus, fadar mulkin kasar, birnin dake fama da dauki ba dadi tsakanin dakarun gwamnati, da na rundunar gwamnatin gabashin kasar mai neman kwace ikon birnin.

A ranar Litinin ne dai majalissar dake lura da harkokin kasashen waje a kungiyar ta EU ta fitar da wata sanarwa, inda ta bayyana damuwa game da tasirin matakan soji da ake dauka a birnin Tirabulus, tana mai cewa matakan soji ba za su iya warware rikicin kasar ba. Kaza lika majalissar ta bukaci sassan biyu da su koma teburin shawarwarin da MDD ke marawa baya.

Gwamnatin Libiyan ta yi na'am da wannan kira, tana mai shan alwashin kawo karshen zaman doya da man ja, tare da fatan kasashen dake taimakawa sojoji tsagin yan adawa za su daina yin hakan, kasancewar matakan sun sabawa kudurorin kwamitin tsaro na MDD.

Har ila yau, majalissar ta yi kira ga kasashen dake da ruwa da tsaki a batun kasar, da su yi nazari kan matakan da suke dauka, wadanda suka sabawa dokokin kasa da kasa, musamman masu nasaba da burin da ake da shi na wanzar da tsaro da zaman lafiya, da daidaito a kasar ta Libiya, da ma yankin da take ciki baki daya. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China