in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
#WayewarKanAsiya#Xi Jinping:Ana bukatar karfin wayewar kai don fuskantar kalubalen da ke gaban duniyarmu
2019-05-15 11:02:25 cri
A yau Laraba, an bude taron tattaunawa game da wayewar kan nahiyar Asiya a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, ban da ci gaban tattalin arziki da kimiyya, 'yan Adam na bukatar karfi daga wayewar kai, don tinkarar kalubale na bai daya da suke fuskanta.

Shugaban ya ce, a halin da ake ciki yanzu na dinga inganta dunkulewar tattalin arzikin duniya, da fasahohin sadarwa, da ma kasancewar nau'o'in al'adu daban daban, 'yan Adam na da kyakkyawar makoma a gabansu. Sai dai ya yi nuni da cewa, ana kara samun rashin tabbas a duniya. A ganinsa, taron ya samar da wani sabon dandali na inganta shawarwari, da musaya, da kuma yin koyi da juna a tsakanin kasashen Asiya da ma sauran kasashen duniya. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China