in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Algeria ta gayyaci kamfanonin kasar Sin su taimaka wajen baza komar tattalin arzikinta
2019-05-15 10:58:23 cri
Ministan kula da harkokin kudi na Algeria, Mohamed Loukal, ya gayyaci kamfanonin kasar Sin, su taimaka wajen baza komar tattalin arzikin kasar da ta dogara kan man fetur.

Da yake ganawa da Jakadan Sin a Algeria; Li Lianhe, Mohamed Loukal, ya yabawa gudunmuwar da kamfanonin kasar Sin suka bayar wajen ginin manyan ayyuka a kasar.

A nasa bangaren, Jakadan na Kasar Sin da ya fara aiki a Algeria cikin watan Disamban bara, ya ce aikinsa shi ne, bunkasa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, musamman ta hanyar bunkasa zuba jari da aiwatar da ayyukan hadin gwiwa.

A watan Oktoban bara ne tsohon ministan kula da masana'antu da ma'adinai na Algeria Youcef Yousfi, ya bayyana fatan gaggauta tattaunawa kan yadda za a taimakawa kamfanonin kasar Sin zuba jari a bangarori daban-daban na kasar, wadanda suka hada da masaku da karafa da laturoni da hakar ma'adinai. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China