Al'ummar Namibia sun cika filin Augasto Neto makil, mai cike da tarihi da aka sanyawa sunan tsohon shugaban kasar, wanda ke birnin Windhoek, domin tsere don murnar cikar shugaban kasar na farko Sam Nujoma shekaru 90 da haihuwa.
Tseren ya kunshi na kilomita 5 da km 10 da kuma km 25 domin kowa ya samu shiga.
Yanzu Sam Nujoma ya bi sahun Shugaban kasar Zimbabwe na farko Robert Mugabe da takwaransu na Zambia Kenneth Kaunda, cikin wadanda suka kai shekaru 90 da doriya da ake damawa da su a bangaren siyasar kungiyar raya yankin kudancin Afrika.
Yadda mutane masu launinka fatan daban daban suka fito a jiyan, ya alamta rayuwar daya daga cikin masu fafutukar 'yancin Namibia, wanda ya sadaukar da rayuwarsa ga samar da adalci ga zamantakewar al'ummar Namibia da suka fito daga bangarori daban daban. (Fa'iza Mustapha)