in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta damke mutane 170 da ake zargi da laifin garkuwa da mutane
2019-05-11 16:31:05 cri
Jami'an tsaro a Najeriya sun yi nasarar damke mutane 170 da ake zargi da yin garkuwa da mutane a manyan hanyoyin kasar a lokacin samamen da jami'an suka kaddamar na baya bayan nan, wani babban jami'in kasar ne ya bayyana hakan a jiya Juma'a.

Mohammed Adamu, babban jami'in hukumar 'yan sandan Najeriyar ya ce, wadanda aka kama ana zarginsu ne da hannu wajen aikata laifukan garkuwa da mutane da fashi da makamai a sassan Najeriyar, ya bayyana hakan ne a lokacin ganawa da wasu manyan jami'an 'yan sanda a Abuja.

Wata kididdiga ta nuna cewa, jami'an 'yan sandan suna samun galaba a yakin da suke da bata gari a duk fadin kasar, in ji jami'in dan sandan.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China